49. Sabuwar Alkawarin Allah

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 1

Wani mala'ika ya ce wa wata budurwa wanda ake ce da ita Maryamu, zata haifi Dan Allah.Tun tana budurwa Ruhu Mai Tsarki ya lullube ta, ta kuma yi ciki. Ta haifi da ta kuma sa masa suna Yesu. Domin haka, Yesu Allah ne kuma mutum.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 2

Yesu yayi al'ajibai da yawa da suka bada tabbatarwa shi Allah ne. Yayi tafiya akan ruwa, ya lafar da ruwan sama mai iska, ya warkar da mutane marasa lafiya da yawa, ya kori aljannu, ya tada matattu zuwa rai, ya juya dunkulen gurasa biyar da kifi biyu zuwa issashen abinci domin mutane fiye da 5,000.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 3

Yesu kuma babban mallami ne, ya kuma yi magana da iko saboda shi Dan Allah ne. Ya koyar cewa, ya kamata ka kaunaci sauran mutane kamar yadda kake kaunar kanka.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 4

Ya kuma koyar cewa, ya kamata ka kaunaci Allah fiya da yadda zaka kaunaci sauran abubuwa, harma da dukiyar ka.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 5

Yesu yace, mulkin Allah yafi komai a duniya daraja. Abu mafi muhimmanci ga kowa shine ya kasance a mulkin Allah. Idan zaka shiga mulkin Allah, dole ne a cece ka daga zunuban ka.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 6

Yesu ya koyar cewa wadansu mutane zasu karbe shi su kuma sami ceto, amma wadansu ba zasu karba ba. Ya ce wadansu mutane suna kama da kasa mai kyau. Sun karbi labari mai dadi na Yesu kuma suka sami ceto. Wadansu mutane suna kama da kasa mai tauri dake kan hanya, inda irin maganar Allah ba ya shiga, kuma basa ba da wani amfani. Wadannan mutanen sukan ki sako game da Yesu kuma baza su shiga mulkinsa ba.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 7

Yesu ya koyar da cewa, Allah yana kaunar masu zunubi kwarai. Yana so ya gafarta masu, ya kuma maishe su 'ya'yansa.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 8

Yesu kuma ya gaya mana ce wa Allah ya tsani zunubi. Sa'anda da Adamu da Hauwa'u suka yi zunubi, ya shafi dukkan zuriyar su. Sakamakon haka, kowane mutum a duniya ya yi zunubi, a rabe kuma ya ke da Allah. Domin haka, kowa ya zama abokin gaba na Allah.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 9

Amma Allah ya kaunaci kowa a duniya sosai harma ya bada makadaicin dansa, domin duk wanda ya ba da gaskiya ga Yesu ba za a hukunta shi saboda zunubansa ba, amma zai kasance tare da Allah har abada.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 10

Saboda zunubinka, kayi laifi kuma ka cancanci mutuwa. Ya kamata Allah yayi fushi da kai, amma ya zuba fushinsa akan Yesu amaimakonka. Sa'adda Yesu ya mutu akan giciye, ya karbi hukuncinka.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 11

Yesu bai taba yin zunubi ba, amma ya zabi a hukuntashi, kuma ya mutu a matsayin hadaya cikakkiya domin ya kawar da zunubanka da zunuban kowanne mutum a duniya. Saboda Yesu ya mika kansa hadaya, Allah zai iya gafarta kowanne zunubi, har ma da munanan zunubai.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 12

Ayyuka nagari ba zasu cece ka ba, Babu abinda za ka iya yi ka sami dangantaka da Allah. Yesu ne kadai zai iya wanke zunubanka. Dole ne ka gaskanta Yesu Dan Allah ne, ya kuma mutu akan gicciye maimakon ka, Allah ya kuma tashe shi da rai.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 13

Allah zai cece duk wanda ya bada gaskiya ga Yesu, ya kuma karbe shi a matsayin Ubangijinsu. Amma ba zai ceci ko dayan da bai ba da gaskiya gare shi ba. Ba ya zabi ko kai mai arzikine ko talaka, na miji ko ta mace, tsoho ko matashi, ko inda kake zama. Allah yana kaunar ka kuma yana so ka bada gaskiya ga Yesu domin ya sami dangantaka na kusa da kusa.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 14

Yesu na gaiyatarka ka bada gaskiya gare shi kuma ayi maka baftisma. Ka bada gaskiya Yesu shine Almasihu, makadaicin Dan Allah? Ka bada gaskiya kai mai zunubi ne kuma ka cancanci Allah ya hukunta ka? Ka gaskanta Yesu ya mutu akan gicciye domin ya dauke zunubanka?

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 15

Idan ka bada gaskiya ga Yesu da abinda yayi maka, kai Krista ne! Allah ya fitar da kai daga mulkin Shaidan ta duhu, kuma ya saka cikin Mulkin Allah na haske. Allah ya dauke tsofofin hanyoyin yin zunubin ka, ya kuma baka sabobin hanyoyin yin adalci.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 16

Idan kai Kirista ne, Allah ya gafarta zunubanka saboda abinda Yesu ya yi. Yanzu, Allah na ganin ka a matsayin abokin sa na kusa a maimakon makiyi.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 17

Idan kai abokin Allah ne da kuma bawan Yesu Ubangiji, za ka so kayi biyayya da abinda Yesu yake koya maka. Ko da shike kai Krista ne, za'a iya jarabtar ka yi zunubi. Amma Allah mai aminci ne kuma yace idan ka furta zunubanka, zai yafe maka. Zai baka karfi kayi yaki da zunubi.

49. Sabuwar Alkawarin Allah — illustration 18

Allah yace kayi addu'a, kayi nazarin maganarsa, ka bauta masa tare da sauran Kiristoci, ka kuma gaya wa wadansu abinda ya yi maka. Dukkan wadannan abubuwa za su taimake ka wurin samun dangantaka mai zurfi da shi.

Labari a Littafi Mai Tsarki daga: Romawa 3:21-26, 5:1-11; Yahaya 3:16; Markus 16:16; Kolosiyawa 1:13-14; 2 Korantiyawa 5:17-21; 1 Yahaya 1:5-10

Read in the reader

Free to use, adapt, and share under an open license (CC BY-SA 4.0).